A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza a Tehran, Hujjatul Islam wal Muslimin Sayyid Mujtaba Badri, limamin masallacin Ahbabul Husain (A.S) da ke Isfahanak, a lokacin da yake hira da Kamfanin Dillancin Labaran Hauza a Tehran, ya bayyana lamarin Mubahala a matsayin babbar shaidar alfahari da daukakar mabiya tafarkin Shi'a a tsawon tarihi, inda ya bayyana cewa: "Yankin Najran shi ne kadai yankin da Kirista ke zaune a cikinsa a yankin Hijaz, wanda ke da kauyuka saba'in da ke karkashinsa a kan iyakar Hijaz da Yemen. Annabin Musulunci (S.A.W.W) yayin da yake rubuta wasiku zuwa ga shugabannin gwamnatoci da cibiyoyin addini na duniya, ya aike da wasika zuwa ga Bishop na Najran yana kiransa zuwa ga addinin Musulunci."
Ya jaddada cewa: "Kiristocin sun gudanar da taron shawara tare da aiko da wakili zuwa Madina domin bincikar hujjojin annabcin Annabi (S.A.W.A). Sai dai a wannan tattaunawa ba su gamsu ba, kuma suka bukaci a gudanar da Mubahala (tsine wa juna domin gano gaskiya)."
Limamin masallacin na Ahbabul Husain (A.S) da ke Isfahanak a Tehran, yayin da yake nuni da cewa Allah ya umarci Annabi (S.A.W.A) da ya yi mubahala da mutane masu adawa da gaskiya ta hanyar saukar da Ayar Mubahala, ya tunatar da cewa: "Bisa shawarar Annabi (S.A.W.W) da Kiristocin Najran, an amince a gudanar da la'anta da mubahala ga makaryaci a wani lokaci da aka kayyade."
Mubahalar Annabi (S.A.W) Da Kiristocin Najran Tana Cikin Abubuwan Al'ajabi Na Tarihin Musulunci
Hujjatul Islam wal Muslimin Badri, ya sake jaddada cewa mubahalar Annabi (S.A.W.A) da Kiristocin Najran tana cikin abubuwa masu ban sha'awa da ban mamaki a tarihin Musulunci, inda ya ce: "An gudanar da taron Mubahala a wani wuri a wajen garin Madina tare da halartar Ahlul Baitin Annabi (S.A.W.W), inda Bishop na Najran ya amince da gaskiyarsu bayan ya ga fuskoki masu haske na wadannan mutane."
Ya yi nuni da furucin babban limamin cocin Najran na amincewa da gaskiyar Ahlul Baiti (A.S) inda ya ce: "Ina ganin wasu fuskoki wadanda idan suka daga hannayensu suka roƙi Allah da ya tumbuke mafi girman duwatsu daga gurbinsu, nan take za a amsa addu'o'insu." Ya kara da cewa: "A cikin dukkan musulmi, babu rayuka masu tsarki da imani mai karfi kamar na Ahlul Baiti (A.S), wanda hakan ya sa tawagar Kiristocin suka janye jiki daga mubahalar bayan gargadi daga shugabanninsu."
Wannan malami na makarantar Hauza ta Tehran, ya dogara da bayanan Allamah Tabataba'i inda ya ce: "Mubahala tana daya daga cikin mu'ujizoji madawwama na Musulunci, kuma kowane mutum mai imani yana iya yin koyi da Annabin Musulunci wajen yin mubahala da mai adawa da shi domin tabbatar da wata gaskiya ta Musulunci, tare da roƙon Allah Ubangijin talikai da ya hukunta su kuma ya kaskantar da su." Ya kuma bayyana cewa: "Saukar Ayar Wilayah a kan matsayin Imam Ali (A.S) da kuma bayar da zobe ga mabuƙaci da ya yi a lokacin sallah, suna cikin abubuwan da suka faru a wannan rana mai cike da daukaka."
Ayar Mubahala Tana Da Tasiri Sosai Wajen Yada Al'adun Wilaya Da Imamanci
Limamin masallacin Ahbabul Husain (A.S) da ke Isfahanak a Tehran ya ce: "Bugu da kari, a kan batun aƙidar hakkin Wilayar Ahlul Baiti (A.S), Ayar Mubahala tana da tasiri sosai; Ma'ana, idan muka ƙaddara cewa dukkan sahabban Annabi (S.A.W.A) suna a matsayi mafi daukaka, babu daya daga cikinsu da yake matsayin 'ran Annabi' (Nafs), amma Ali (A.S) shi ne ran Annabi. Don haka, babu wani da zai iya samun ɗaukaka a kan Ali (A.S)."
Wannan malami na makarantar Hauzar Tehran ya tunatar da cewa: "Idan muka yi imani da wannan batu kuma muka amshi jagorancin bincike na Amirul Muminina Ali (A.S) ga duniyar Musulunci ta yau, wannan yana nufin mun yaɗa ingantaccen Musulunci na gaskiya a daukacin duniya; A lokacin ne za a iya dakatar da bidi'o'i da karkacewa kamar Wahabiyanci da Baha'iyanci da makamantansu, kuma ingantacciyar aƙida mai tsarki za ta bazu a cikin al'umma."
Yayin da yake bayyana cewa yaɗa gaskiyar wannan lamari na tarihi na Mubahala ya zama wajibi ga kowane mai wa'azin addini, ya kammala da cewa: "Albarkar wannan lamari na Alkur'ani tana da tasiri sosai wajen tabbatar da gaskiyar Ahlul Baiti (A.S)."
Ra'ayinka